Jami’an tsaro sun buqaci agaji wajen kame masu sojan gona
Kwamitin tsaro na Jihar Legas da ya hada da rundunonin rukunonin soja da ’yan sanda, a taronsu na wata-wata, sun bukaci jama’ar gari su rika ba da tasu gudunmuwa wajen tafiyar da harkokin tsaro, musamman wajen fallasa mutanen da ke sojan gona.Da yake wa taron manema labarai jawabi, jim kadan da kammala taron, kwamamdan sojan […]
Kwamitin tsaro na Jihar Legas da ya hada da rundunonin rukunonin soja da ’yan sanda, a taronsu na wata-wata, sun bukaci jama’ar gari su rika ba da tasu gudunmuwa wajen tafiyar da harkokin tsaro, musamman wajen fallasa mutanen da ke sojan gona.
Da yake wa taron manema labarai jawabi, jim kadan da kammala taron, kwamamdan sojan sama, mai kula da bataliya ta 9 da ke unguwar Ikeja, Birgediya-Janar Adeniyi Oyebade ya ce samar da tsaro ba aiki ne na gwamnati kadai ba, ko kuma masu saye da kayan sarki, kowane dan kasa na da rawar da zai taka wajen ingata matakan tsaro.
Kwamandan ya ce daya daga cikin manya-manyan kalubalen da jami’an tsaro ke fuskanta, musamman a Jihar Legas, sau tari sai ka taras da mutane sanye da kayan sarki suna sojan gona, suna aikata ayyukan assha.,
Ya ce sau tari sukan kama mutane masu ikirarin ma’aikatan tsaro ne, amma da an zurfafa bincike, sai ka taras karya suke yi, masu sojan gona ne. “Gwamnatin Legas na kokari wajen yakar ayyukan ta’addanci wajen taimaka wa jami’an tsaro da dukkan abin da zai inganta aikinsu, lamarin da ke kara wa jami’an kwarin gwiwar gudanar da ayyukansu. Taron manema labarai da ake yi wata-wata yana agazawa wajen sanar da jama’a irin rawar da ake bukatar su taka game da harkokin tsaro”. Inji shi.
Kwamanda Oyebade yace da taimakon naurar zamani irin su wayan salula mutane na iya daukan hoton duk wani mai sanye da kayan sarki da suke tuhumar cewa sojan gona ne, kuma idan suka gane cewa sojan gaskiya ne amma irin shigar da yayi baiyi kama da na maaikacin sarki ba to zai huskanci hukunci dai dai da yadda dokar soja tace a hukunta wanda ya wulakanta kayan sarki.
Dangane da inda sojan gonar ke samun kayan sarki, kwamandan ya ce da yawansu suna saye ne hannun ’yan fasa-kwabri. An nuna wa manema labarai kayayyakin sarki iri daban-daban da kuma lokacin da ake sa kowanne daga cikinsu.
Shi ma da yake tofa albarkacin bakinsa, kwamandan rundunar sojan sama mai kula da sashe na 435, Kwamando Sunday Wukangha ya bayyana yadda kowanne soja ya kamata ya sa mukaminsa. Idan aka samu kuskure a wajen rataya mukamin, ana iya gane cewa sojan gona ne, ana iya damke shi ko kuma a dauki hotonsa, a mika wa ’yan sanda, wadanda za su gudanar da bincikensu.