Jami’an tsaro sun tarwatsa zanga-zangar da ta ɓarke a Kano

Kawo yanzu dai ba a gano dalilin zanga-zangar da ta ɓarke a ƙarƙashin Gadar Ƙofar Nasarawa ba.

Jami’an tsaro sun tarwatsa zanga-zangar da ta ɓarke a Kano

Jami’an tsaro da suka haɗa da ’yan sanda da DSS sun tarwatsa zanga-zangar da ta ɓarke a Ƙofar Nasarawa da ke Jihar Kano.

Bayanai sun ce masu zanga-zangar sun yi dandazo a ƙarƙashin gadar Ƙofar Nasarawa, lamarin da jami’an tsaron suka yi musu tarnaƙi da barkonon tsohuwa.

Kawo yanzu dai ba a gano dalilin gudanar da zanga-zangar ba, sai dai tuni jami’an tsaro suka sanya shamaki a hanyoyin da ke daura da zuwa Gidan Gwamnatin Kano.

Mai magana da yawun rundunar ’yan sandan Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya ce ƙura ta lafa kuma kawo yanzu sun cafke mutum 17 da ake zargi na da hannu a lamarin.

Na gaji bashin 8.9bn a matsayin shugaban APC — Ganduje

Boko Haram sun sace mutum 2 da kayan abinci a Borno

Buhari da El-Rufai ba su halarci babban taron APC ba

Ƙungiya ta raba wa marayu da mabuƙata kayan makaranta a Kano