Jarumin fim din Hausa Malam Waragis ya rasu
Allah Ya yi wa jarumin fim din Hausa Malam Muhammad Umar Jos wanda aka fi sani da Malam Waragis ya rasu a garin Jos da ke Jihar Filato. Al’amin Ciroma ya wallafa a shafinsa na facebook cewa jarumin ya rasu ne bayan ya yi fama da jinya na tsawon lokaci. Tuni aka […]

Allah Ya yi wa jarumin fim din Hausa Malam Muhammad Umar Jos wanda aka fi sani da Malam Waragis ya rasu a garin Jos da ke Jihar Filato.
Al’amin Ciroma ya wallafa a shafinsa na facebook cewa jarumin ya rasu ne bayan ya yi fama da jinya na tsawon lokaci.
Tuni aka yi jana’izar mamacin a garin Jos kamar yadda shara’ar musulunci ta tanadar.