Jikar tsohon shugaban Afirka ta Kudu Nelson Mandela ta rasu
Zoleka, jikar jagoran gwagwarmayar samun ’yancin kasar Afirka ta Kudu, Nelson Mandela, ta rasu tana da shekaru 43.

Zoleka, jikar jagoran gwagwarmayar samun ’yancin kasar Afirka ta Kudu, Nelson Mandela, ta rasu tana da shekaru 43.
A safiyar Talata ne iyalan Mandela suka sanar da rasuwar Zoleka bayan fama da cutar kansa.
- An harbi dalibai 3 an sace wata a Kwalejin IMAP da ke Nasarawa
- Tuna baya: Tarihin Dokta Goodluck Ebele Jonathan
Kakakin iyalan, Zwelabo Mandela, ya ce a ranar Litinin ta je asibiti domin ganin likita, inda daga bisani “rai ya yi halinsa a gaban ’yan uwa da abokan arziki.”
Ya ce a baya-baya nan, cutar “ta yi mata illa a kwakwalwarta da lakarta, da kuma hanta da huhu da kuma kashin baya.”
Marigayiya Zoleka, ’ya ce ga ’yar autar Mandela, Zindzi da mijinta na farko Zwelibanzi Hlongwane.