Kada wanda ya kafa allunan taya ni murnar zama Minista – Wike

Ya ce aikin gina birnin ne yanzu a gabansa

Kada wanda ya kafa allunan taya ni murnar zama Minista – Wike

Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya hana karkafa duk wasu allunan talla da nufin taya shi murnar zama Minista.

A cikin wata sanarwa da Daraktan Yada Labarai na ma’aikatar, Anthony Ogunleye, Wike ya ce ya yanke shawarar daukar matakin ne saboda nuna kishin kasa da kuma mayar da hankali wajen aikin da Tinubu ya sa shi.

Sanarwar ta ce Ministan ya gode da fatan alherin, amma ya bukaci a dakatar da amfani da irin wadannan allunan tallan.

Wike ya ce babban burinsa shi ne ya bunkasa Abuja ta yadda mazauna cikinta za su ji dadin zamanta a zamanin mulkinsa.

Ya kuma ce ya yana matukar girmamawa da kuma mutunta bukatun mazauna birnin tare da jajircewa wajen ganin ya biya musu su.

Shugaban Dattawan Arewa ya ajiye sarautar Magajin Rafin Zazzau

Tinubu ya sanya dokar ta-baci a Jihar Ribas

Hamas ta ɗora alhakin harin da Isra’ila ta kai a kan Amurka

Majalisar Wakilai ta amince da ƙudirin dokar haraji