Kamfanin MTN ya ba wasu makarantu gudunmawar kayan aiki a Legas
Kamfanin MTN ya baiwa makarantu 2, makarantar Oriwu model junior/secondary da kuma makarantar Orewo junior/senior grammer da ke cikin karamar Hukumar Ikorodu gudunmowar kujerin dalibai da na malamai da littafan rubutu da kuma gwagwanayen tarkacen kayan lissafi (math set) da riguna ruwan dalibai. Da take karbar kayayyakin, a madadin gwamnatin Jihar Legas, Kwamishinar Ilimi, Misis […]
Kamfanin MTN ya baiwa makarantu 2, makarantar Oriwu model junior/secondary da kuma makarantar Orewo junior/senior grammer da ke cikin karamar Hukumar Ikorodu gudunmowar kujerin dalibai da na malamai da littafan rubutu da kuma gwagwanayen tarkacen kayan lissafi (math set) da riguna ruwan dalibai.
Da take karbar kayayyakin, a madadin gwamnatin Jihar Legas, Kwamishinar Ilimi, Misis Olayinka Oladunjaiye ta yi na’am da abubuwan alherin da kamfanin na MTN ya saba yi wa jihar, musamman a fannin ilimi.
Kwamishinar ta ce ilimi ya fi karfin gwamnati ita kadai, muddin ana son ba da wadataccen ilimi ga yara, akwai bukatar kamfanoni masu zaman kansu da ma masu hannu da shuni su ba da tallafinsu.
Da yake jawabinsa wajen mika kayayyakin, shugaban kula da fannin ilimi na kamfanin na MTN, Mista bictor Orie Ononogbu ya ce wannan kadan ne daga cikin abin da kamfanin ya yi ko kuma zai ci gaba da yi wa fannin ilimi a Jihar Legas da ma sauran jihohin Najeriya.
Ya ce duk mazaunin Jihar Legas yana ganin abin da gwamnati ke yi a fannin ilimi da ma sauran fannonin rayuwa daban-daban don haka bai dace a bar gwamnati da wannan aiki ita kadai ba.
Su dai wadannan makarantun sun samu kujerin dalibai 200 ne kowannensu, kana guda 20 na malamansu, yayin da takardun rubutu da gwangwanayen kayan lissafi da rigar ruwa na daliba masu yawan gaske, wadanda aka kiyasta kudinsu ya kai Naira miliyan 10.