Kamfanonin jirage sun dakatar da ayyuka kan tsadar mai
Tsadar man ta sanya kamfanonin fitar da sanarwar dakatar da ayyukansu.
Wani Jirgin Sama yayin da ya ke shan mai
Matsalar karancin mai ta tilasta wa kamfanonin jiragen sama a Najeriya dakatar da ayyukansu.
Kamfanonin sufurin jiragen sama sun kara farashin tikitinsu a kwanakin baya.
- Tsohon dan kwallon Najeriya Justice Christopher ya rasu
- Rikicin Ukraine: Romaniya za ta bai wa ’yan Najeriya gurabun karatu
A ranar kamfanonin sun ce sun yi mamakin ganin karin farashin man jirgin sama, inda aka sayar da lita a kan Naira 607 a Kano.
Wannan ya nuna an kara fiye da Naira 100 cikin kwana guda.
Aminiya ta rawaito cewa wasu masu kamfanoni sufurin jiragen sama sun samu sanarwar daga dillalan man a ranar Talata cewa farashin man JetA1 ya karu zuwa Naira 597 a Legas, Naira 599 a Abuja da Fatakwal, da kuma Naira 607 a Kano.
A ranar Litinin an sayar da man a kan Naira 470 ne a Legas, a Kano kuma Naira 495.
Hakan ya janyo tsaiko ga tashin jiragen sama a manya da kananan filayen jirgin sama na Najeriya a ranar Laraba.
Yawancin kamfanonin sufurin jiragen saman sun fitar da sanarwar da ke bayana halin da su ka shiga tara da ba wa abokan fasinjojinsu hakuri.
Fasinjoji a filayen jiragen saman kasar nan sun shiga rusu kan rashin samun jiragen da za su yi jigilarsu.