Kano: Daliban JSS1 da SS1 sun koma makaranta

Kwamishinan ilimin jihar Muhammad Sunusi Kiru ne, ya bayyanawa cewa daliban su koma ranar 16 ga watan Nuwamba.

Kano: Daliban JSS1 da SS1 sun koma makaranta

A yau ne daliban aji daya (JSS1) na karamar sakanda da babbar sakandare (SS1) suka koma makaranta a jihar Kano.

Kwamishinan Iliminjihar, Muhammad Sanusi Kiru, ya sanar da hakan a sanarwar da Jami’in Hulda da Jama’a na ma’aikatar Aliyu Yusuf fitar.

“Ya kamata daliban makarantun Firamare 1-6 su sake komawa gaba daya daga ranar Litinin, 16 ga Nuwamba, sabanin umarnin farko da aka sanya musu ranakun zuwa makaranta”, inji shi.

Ya yi kira ga iyayen da yaransu ke wadannan azuzuwan da su yi biyayya ta hanyar dawo da su a ranakun da aka sanya.

Daga nan sai kwamishinan ya umarci daraktoci da shugabannin makarantu da sauran masu ruwa da tsaki da su kasance cikin shiri don ci gaba da aikin.

Idan ba a manta ba, gwamnatin jihar ta umurci daliban JSS-1 da SS-1 da su kasance a gida na tsawon makonni biyar domin an kammala jarabawar masu kammala karama da babbar sakandare. 

Boko Haram sun ƙone makarantu a Borno

Har yanzu ’yan bindiga ba su saki matar Manjo Janar Rabe ba

An binne gawar Manjo Janar Rabe a Katsina

Wasu tsiraru ne ke rura matsalar tsaro a Najeriya — Christopher Musa