Karanci da tsadar man fetur sun kunno kai a Abuja

Karancin man fetur ya kunno kai a Birnin Tarayya, Abuja, da kewaye a ranar Talata

Karanci da tsadar man fetur sun kunno kai a Abuja

PIC.4. FUEL HAWKER POPULARLY KNOWN AS BLACK MARKETERS HAVING A FIELD DAY AT FADEYI
AREA OF LAGOS ON THURSDAY (21/5/15) .
2673/21/5/2015/JAU/NAN

Karancin man fetur ya kunno kai a cikin Birnin Tarayya, Abuja, da kewaye a ranar Talata.

Yanayin ya sa gidajen mai da dama kullewa tare da haifar tsadar man fetur a garin.

Kakakin Kamfanin Mai na Kasa (NNPC), Kennie Obateru, ya danganta karancin man da zanga-zangar #EndSARS, amma ya ba da tabbacin cewa mai zai wadatu a ranar.

Obateru ya ce ’yan kasuwa da dama sun fara samun lodin man da zai kawar da karancinsa.

A zagayen gari da Aminiya ta yi, ta gano matsaloli a yadda ake sayar da man a wasu gidajen mai a Abuja.

A gidan man NNPC na Area 10, kofar daya aka bude da motoci na gwamutsuwa wajen shiga, wanda hakan ya haddasa cunkoso.

A gidan man Total ma ba ta sauya zani ba, sai kuma ’yan bunburutu da suka cika wurin suna sayar wa masu motoci da tsada.

Wakilinmu ya ga ’yan bunburutun na sayar da galan mai cin Lita 4 a kan N1,000 zuwa N1,200

A gidan Man A.A Rano da ke Jabi kuma, wakilinmu ya ga cinciridon ababen hawa na kokarin shan mai.

Lamarin bai canja ba a gidan man NIPCO da ke Jabi inda shi ma aka cika shi makil.

Zanga-zangar #EndSARS dai an fara ta ne cikin lumana amma daga baya ta rikide zuwa rikici bayan zauna-gari-banza sun shiga ciki suna kone-kone da satar dukiyoyin gwamnati da na al’umma.

Daga baya bata-gari sun rika fasa rumbunan gwamnati da aka ajiye kayan tallafin COVID-19 suna kwashewa.

Kungiyar Manya ’Yan Dillalan Man Fetur ta Najeriya (MOMAN), ta ce ba za ta yi magana kan lamarin ba.

Boko Haram sun ƙone makarantu a Borno

Har yanzu ’yan bindiga ba su saki matar Manjo Janar Rabe ba

An binne gawar Manjo Janar Rabe a Katsina

Wasu tsiraru ne ke rura matsalar tsaro a Najeriya — Christopher Musa