karancin mai: DPR ta rufe gidajen mai 39 a Kano

Sashen kula da albarkatun man fetur watau DPR  ya rufe  gidajen mai 39  cikin makonni biyu a Jihar Kano saboda samun su  da laifin sayar da mai sama  da farashin da doka ta tanada.Jami’in sashen mai kula da shiyyar Kano, Alhaji Isa Tafida ne ya sanar da haka ga manema labarai  ranar Talatar da ta […]

karancin mai: DPR ta rufe gidajen mai 39 a Kano
karancin mai: DPR ta rufe gidajen mai 39 a Kano

Sashen kula da albarkatun man fetur watau DPR  ya rufe  gidajen mai 39  cikin makonni biyu a Jihar Kano saboda samun su  da laifin sayar da mai sama  da farashin da doka ta tanada.
Jami’in sashen mai kula da shiyyar Kano, Alhaji Isa Tafida ne ya sanar da haka ga manema labarai  ranar Talatar da ta gabata, a karshen zagayen da ya yi don duba yadda ake sayar da mai a fadin jihar.
Alhaji Isa Tafida ya bayyana cewa za a ci gaba da rufe gidajen mai muddin dai suna karya dokar sayar da shi ko boye shi da nufin cin kazamar riba.
Matsalar albarkatun  man fetur ta dade tana addabar al’umar kasar nan, kuma masu ruwa da tsaki suna bakin  kokarin su wajen ganin al’amurra sun gyaru  amma wasu tsiraru suna yin zagon kasa ga kokarin da ake yi na kawar da wannan matsala ta man fetur.
Sai dai mafiya yawan al’umomin da Aminiya ta zanta da su  watau direbobi da masu yin tafiye-tafiye  sun bayyana  cewa ya kamata a rika yin horo mai tsanani kan duk wanda aka samu da laifin boye man.