KAROTA ta kama jabun magunguna na Naira miliyan 50

Mun samu nasarar cafke jabun magungunan ne a kan titin Murtala Mohammed da ke birnin Kano.

KAROTA ta kama jabun magunguna na Naira miliyan 50

Hukumar Kula da Zirga-Zirgar Ababen Hawa ta Kano (KAROTA) ta ce jami’anta sun samu nasarar cafke jabun magunguna na fiye da miliyan 50 a jihar.

Wannan dai na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar, Nabulisi Abubakar Kofar Na’isa ya fitar.

A cewarsa, hukumar ta samu nasarar cafke jabun magungunan ne a kan titin Murtala Mohammed da ke birnin Kano “lokacin da direban motar yake ƙoƙarin shiga kasuwar Sabon Gari domin rabawa masu shaguna.

“Daga cikin magungunan da aka cafke sun hada da: maganin ciwon jiki, maganin zazzaɓi, maganin tari da sauran su.”

Shugaban Hukumar KAROTA, Faisal Mahmud Kabir ya ce hukumar ba za ta zuba ido ta bari ana ta’ammali da miyagun kwayoyi a Jihar Kano ba.

Ya ja hankalin al’umma da su guji sayen magani a wajen da bai karanta ba domin gujewa fadawa cikin matsala.

Ya ce ƙofar hukumar a buɗe take wajen karɓar bayanan sirri domin daƙile yawaitar jabun magani a faɗin jihar nan baki daya.

Zaɓen Edo: Abin da ya kai ni Ofishin INEC — Obaseki

An kama matan da suka yi yunƙurin sayar da tagwayen jarirai a Legas

Mazauna gaɓar Kogin Benuwe sun soma ƙaurace wa gidajensu

Zaɓen Edo: Yadda ’yan sanda suka fitar da Gwamna Obaseki daga ofishin INEC