KAROTA za ta dauki karin ma’aikata
Hukumar KAROTA za ta dauki karin jami’ai da za ta tura zuwa sabbin masarautun Jihar Kano.
Jami’an hukumar KAROTA
Hukumar Kula da Ababen Hawa ta Jihar Kano (KAROTA) za ta dauki sabbin ma’aikata 700, dominkara wa jami’ai 2,500 da take da su a Jihar karfi.
Manajan Daraktan Hukumar, Baffa Dan’agundi, ya za a tura sabbin jami’an ne su yi aiki a sabbin masarautun Bichi, Gaya, Karaye da Rano domin tabbatar da kiyaye dokokin ababen hawa.
- ‘Ciyar da daliban Kano kan lakume N4bn duk shekara’
- Gwamnan Jigawa ya gabatar da kasafin 2021
- Yadda Najeriya za ta bunkasa kasuwanci da fasahar zamani — NITDA
Dan’agundi ya kuma gargadi ‘yan talla da ke neman dawowa kan tituna da sauran wuraren da aka haramta yin hakan a birnijn Kano.
“Mun tsananta domin ganin ‘yan tallan da aka tayar ba sake dawowa suna haddasa wa masu amfani da tituna matsala ba”, inji shi.
A cewarsa, nan gaba hukumarsa za ta yi hadin gwiwa da Hukumar Kula da Hanyoyi ta Jihar Kano (KARMA) domin gyaran tituna da ke cikin birnin Kano da kewaye.