Kashi 70 na dalibai ne suka fadi jarrabawar shiga makarantun gaba da sakandare a bana
A cikin kashi 100 na daliban da suka zauna jarrabawar shiga makarantun gaba da sakandare, an bayyana cewa kashi 70 ne suka fadi wannan jarrabawar, musamman ma idan aka kwatanta shi da yawan wadanda ba su ci jarrabawar Turanci da lissafi ba.Da yake wa taron manema labarai bayani a birnin Ikko, shugaban hukumar jarrabawa ta […]
A cikin kashi 100 na daliban da suka zauna jarrabawar shiga makarantun gaba da sakandare, an bayyana cewa kashi 70 ne suka fadi wannan jarrabawar, musamman ma idan aka kwatanta shi da yawan wadanda ba su ci jarrabawar Turanci da lissafi ba.
Da yake wa taron manema labarai bayani a birnin Ikko, shugaban hukumar jarrabawa ta kasasashen yammacin Afirka, Mista Charles Egurida ya ce a wannan shekarar, daliban da yawansu ya kai kusan dubu dari 3 ne suka zauna wannan jarabawar, amma wadanda suka yi nasarar samun abin da ake bukata a matakin farko na shiga makarantun gaba da sakandare, su dubu 160 da ’yan kai ne, wadanda su ma din ba lissafi da Turanci.
Ya ce idan aka hada da wadanda suka samu Turanci da lissafi, yawansu bai haura dubu 86 ba, lamarin da ya nuna ke nan kashi 29 da digo 17, wanda ya yi daidai da kashi 70 da digo 83 ke nan suka fadi warwas.
Mista Eguridu ya ce idan aka kwatanta faduwar wannan shekarar da shekaru biyu da suka gabata, sai a ga cewa na wannan shekarar ya fi muni domin ko a shekarar 2011 daliban da yawansu ya kai kashi 36 da digo 7; kana a shekarar 2012 an sami kashi 37 da digo 97 suka samu nasarar cin jarrabawan ciki ko har da lissafi da Turanci, wadanda su ne kashin bayan jarrabawan da kuma samun damar shiga makarantun gaba da sakandare.
Sai dai Mista Eguridu ya ce akwai jarrabawar daliba da aka rike, biyo bayan samunsu da magudi daban-daban kuma hukumar tana da kwamiti mai duba wannan, ta dauki matakin da ya dace kafin ta sanar da makarantun daliban.
Shugabam hukumar jarabawan ya ce a bisa binciken da suka gudanar na dalilan da ke sa dalibai na yawan faduwa jarabawa, shi ne wasu daga cikin su sun hada da rashin baiwa fannin ilmi fifikon da ya dace daga gwamnati, musamman abin da ya shafi kudi, sai kuma rashin wadatattun kayan aikin koyarwa, kana iyaye suna nuna halin ko-oho ga ilimin ’ya’yansu.
Ya ce bai yiwuwa a ce a bar malamai da kashin mahaukacin kare.