Kirsimeti: NSCDC Ta Girke Jami’ai 780 A Gombe

Hukumar Sibil Difens ta girke jami’anta 780 domin bikin Kirsimeti da Sabuwar Shekara a Gombe

Kirsimeti: NSCDC Ta Girke Jami’ai 780 A Gombe

Dakarun Rundunar ta Musamman ta mata zalla da NSCDC ta kafa. (Hoto: @raufaregbesola).

A kokarinta na kare rayuka da dukiyoyi Gombe, Hukumar Tsaron Farin Kaya (NSCDC) ta girke jami’ai 780 domin sintiri a Jihar Gombe a lokacin bukukuwan kirsimeti da sabuwar Shekara.

Kwamandan hukumar a jihar, Muhammad Bello Mu’azu, ne ya sanar da hakan, yana mai umurtar Kwamandojin Yankin da na Kananan hukumomi da sauransu cewa su tabbatar sun tura isassun jami’ai a lungu da sakon jihar.

A cewar sanarwar, za a tura jami’an ne a wuraren ibada da kasuwanni da tashohin mota da kuma wuraren shakatawa.

Sannan sai ya bukaci jama’a da su yi bukukuwan a tsanake wajen kiyaye doka da oda domin jami’ansa za su yi aikinsu ba sani, ba sabo.

A cewarsa, za su tabbatar da ganin sun tsare rayuka da dukiyoyi yadda ya dace kafin lokacin kirsimeti da kuma Sabuwar Shekara.

An harbe ’yan sanda biyu a Yobe

Netanyahu ya bai wa Hamas wa’adin sakin Isra’ilawan da take garkuwa da su

Gwamnatin Kano za ta kafa hukumar kula da masu buƙata ta musamman

‘Nijeriya ce ƙasa ta 140 mafi rashawa a Duniya’