Ko ni na tambaye ka kyautar fili a Abuja kar ka ba ni – Tinubu ga Wike
Tinubu ya bukaci shi ya mayar da hankali wajen farfaɗo da martabar Abuja

Shugaban Kasa Bola Tinubu, ya bukaci Ministan Abuja, Nyesom Wike, da kada ya kuskura ya ba kowa kyautar fili a Abuja, ko da shi da kansa ne ya tambaya.
A maimakon haka, shugaban ya bukaci Wike ya dage wajen sake farfado da martabar Abuja a matsayin hamshakin birni abin alfahari.
- EFCC ta fara binciken shugaban hukumar yaki da cin hanci ta Kano
- Sabuwar hukumar hana yaduwar makamai za ta dauki mutum 300,000 aiki
Tinubu ya bayyana hakan ne lokacin da yake jawabi yayin bude taron shekara-shekara na Kungiyar Lauyoyi ta Najeriya (NBA) a Abuja, ranar Lahadi.
Shugaban ya kuma bayyana Wike a matsayin “Uban-dakin Abuja.”
“Ina so ka mayar da hankalinka wajen sake fargado da martabar Abuja. Ko Ni na nemi kyautar fili a wajensa, kada ka ba ni,” in ji Tinubu.
Wike, wanda dan jam’iyyar PDP ne dai na daya daga cikin ministoci 45 din da Tinubu ya rantsar a makon da ya gabata.