Ko samun kujerar kwamitin tsaro ta Majalisar dinkin Duniya da Najeriya ta yi zai amfani kasar da al’ummarta?

A makon da ya wuce ne Najeriya ta samu zama daya daga cikin membobin kwamitin tsaro na Majalisar dinkin Duniya, a yayin da kasar Saudiyya ta ce ba ta bukatar wannan kujera da aka ba ta. Abin tambaya a nan shi ne, shin ko wannan kujera za ta zama mai amfani ga Najeriya da al’umarta? […]

Ko samun kujerar kwamitin tsaro ta Majalisar dinkin Duniya da Najeriya ta yi zai amfani kasar da al’ummarta?
Ko samun kujerar kwamitin tsaro ta Majalisar dinkin Duniya da Najeriya ta yi zai amfani kasar da al’ummarta?

A makon da ya wuce ne Najeriya ta samu zama daya daga cikin membobin kwamitin tsaro na Majalisar dinkin Duniya, a yayin da kasar Saudiyya ta ce ba ta bukatar wannan kujera da aka ba ta. Abin tambaya a nan shi ne, shin ko wannan kujera za ta zama mai amfani ga Najeriya da al’umarta? Ga abin da mutane suka bayyana ta hannun wakilanmu na sassan kasar nan:

Al’amarin yana da kyau ga Najeriya
 – Abdulwasi Salawuddin
Abdulwasi Salawuddin: “Samun Najeriya ta shiga cikin wannan kwamitin yana da kyau kwarai da gaske, domin da sako take bayarwa amma yanzu tana ciki ne tsumbul, ba wata kumbiya-kumbiya da za a yi ba da saninta ba, kuma daga yanzu batun wani ya yi magana a madadinta ya kau, sai dai ta tsaya wa kanta kuma har ta tsaya wa wata kasar; sabanin abin da ke faruwa a da. Ka ga da sako take bayarwa amma yanzu sai dai wata kasa ko kasashe su raba da ita kuma da ma ita ce babbar kasa mai tasiri a nahiyar Afrika. Ni dai a nawa ra’ayin yana da amfani kwarai da gaske.”