Kofin Duniya 2026: Yadda kasashen Afirka za su fafata wajen neman tikiti

Najeriya da Afirka ta Kudu da Benin da Zimbabwe da Rwanda da Lesotho na rukuni daya.

Kofin Duniya 2026: Yadda kasashen Afirka za su fafata wajen neman tikiti

Hukumar Kwallon Kafa ta Afirka CAF a madadin FIFA ta fitar da jadawalin wasannin neman gurbi a gasar Kofin Duniya bangaren kasashen Afrika.

Jadawalin wanda CAF ta fita a ranar Alhamis a birnin Abidjan na kunshe da kasashe 54 wadanda aka rarraba rukunnai 9 da za su fafata a wasannin gida da waje don fitar da zakaru a cikinsu.

Jadawalin ya nuna cewa rukunin A na kasashen na kunshe da Masar da Burkina Faso da Guinea Bissau kana Saliyo sai Habasha sannan Djibouti.

A rukunin B akwai kasashen Senegal da jamhuriyyar Dimokuradiyyar Congo kana Mauritania sai Togo da Sudan da kuma Sudan ta kudu.

Bangaren rukunin C kuwa ya kunshi kasashen Najeriya da Afirka ta Kudu kana Benin da Zimbabwe sannan Rwanda da Lesotho.

Rukunin D na dauke da kasashen Kamaru da Cape Verde da Angola da Libya sannan Eswatini sai Mauritius.

Rukunin E kuwa akwai kasashen Morocco da Zambia da Congo Brazzaville da Tanzania sai Jamhuriyar Nijar kana Eritrea.

Rukunin F na kunshe da Ivory Coast da Gabon da Kenya da Gambia sannan Burundi sai tsibirin Seychelles.

A Rukunin G akwai kasashen Algeria da Guinea da Uganda da Mozambique kana Bostwana da Somalia.

Jadawalin na CAF na nuna cewa a rukunin H akwai Tunisia da Equatorial Guinea kana Namibia sannan Malawi da Liberia da kuma São Tome and Principe.

Rukunin I kuma na karshe a wannan jadawali na dauke da kasashen Mali da Ghana sannan Magadascar sai Jamhuriyyar Afirka ta Tsakiya sannan tsibirin Comoros kana Chad.