Kotu ta ayyana Minista a matsayin Sanatan Filato bayan soke zabe

Kotun dai ta tabbatar da hukuncin kotun sauraron kararrakin zabe ne

Kotu ta ayyana Minista a matsayin Sanatan Filato bayan soke zabe

Gwamnan Jihar Filato, Simon Lalong a wajen yakin neman zabe

Kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja, ta soke zaben Sanatan Filato ta Kudu a Jihar Filato, Napoleon Bali, sannan ta ayyana Ministan Kwadago, Simon Lalong a matsayin sabon sanata.

Kotun dai ta yanke hukuncin ne a ranar Talata, bayan ta tabbatar da hukuncin kotun sauraron kararrakin zabe wacce ta soke nasarar Bali na jam’iyyar PDP.

Lalong dai ya tsaya takarar ce a karkashin jam’iyyar APC a zaben ranar 25 ga watan Fabrairu, amma bayan an ayyana cewa ya sha kaye a zaben, Shugaban Kasa, Bola Tinubu ya nada shi Minista.

A cewar kotun, jam’iyyar ta PDP ta saba umarnin kotu kan kin shirya manyan taruka a matakan Mazabu, Kananan Hukumomi da Jiha tun a shekara ta 2021.

A sakamakon haka ne kotun ta ce bai halasta PDP ta tsayar da ’yan takara ba a zabukan Jihar.

Kotun dai wacce ke karkashin jagorancin Mai Shari’a E.O Williams-Daeoud, ta ce kotun baya ta yi daidai da ta ayyana dan takarar APC a matsayin wanda ya lashe zaben saboda dukkan tarukan da PDP ta yi a Jihar ba halastattu ba ne.

Matar aure ta banka wa mijinta wuta

Abin da ya sa na yi wa Buhari juyin mulki —IBB

Yadda aka kama ɗan shekara 65 ɗauke da bindiga

Ana zargin malami da azabtar da ɗalibi kan shan mangwaro a makaranta