Kotu ta ba da belin Yahaya Bello kan N500m

Babbar Kotun Tarayya ta bayar da belin tsohon Gwamnan Jihar Kogi Yahaya Bello a kan Naira miliyan 500 a shari’ar zargin sa da karkatar da Naira biliyan 80.

Kotu ta ba da belin Yahaya Bello kan N500m

Yahaya Bello a kotu bayan Hukumar EFCC ta kama shi

Babbar Kotun Tarayya ta bayar da belin tsohon Gwamnan Jihar Kogi Yahaya Bello a kan Naira miliyan 500 a shari’ar zargin sa da karkatar da Naira biliyan 80.

Hukumar Yaƙi da Masu Karya Tattalin Arziƙi (EFCC) ce ta gurfanar da Yahaya Bello kan zargin karkatar da kuɗaɗen a lokacin da yake gwamna.

Mai Shari’a Emeka Nwite ne ya bayar da belin da sharadin tsohon gwamnan zai kawo mutum biyu da za su tsaya masa, kowannensu zai ajiye kwatankwacin wannan kuɗi.

Wajibi ne kowannensu ya mallaki gida a Abuja sannan ya sako wa kotu takardun gidajen domin ta tantance.

’Yan sanda sun kama baƙin haure 165 a Kebbi

Gobara ta yi ajalin almajirai 17 a Zamfara

Saura ƙiris Bello Turji ya zo hannu – Ministan Tsaro

Sarkin Jiwa a Abuja ya yi rashin mahaifiya