Kotu ta ba da belin Sowore a kan N200m
Kotun ta kara da cewa cewa wajibi ne mutanen da za su tsaya wa Sowore su samu tantancewar lauyoyin masu gabatar da kara, Akinlolu Kehinde, (SAN)
Omoyele Sowore
Babbar Kotun Tarayya da ke zamanta a Abuja, ta bayar da belin dan gwagwarmaya, kuma mai kafar yada labarai ta Sahara Reporters, Omoyele Sowore, a kan kudi Naira miliyan 200.
Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS) ce ta gurfanar da Sowore a gaban kotu, kan zargin cin mutuncin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, inda bayyana shi a matsayin “babban mai laifi” a wani sako da dan gwagwarmayan ya wallafa a shafukansa na X da Facebook.
The defendant’s lawyer, R. O. Adakole, however, appealed to the judge that Sowore be released to him to enable him get his passport from the US embassy in Lagos.
Justice Umar then adjourned to July 6, 2026, for continuing of hearing after Sowore’s counsel plea.
A safiyar Talatar nan ce Mai Sharia Umaru Mohammed ya bayar da belin Sowore—dan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar AAC— da sharadin ya kawo mutum biyu da za su tsaya masa.
Alkalin ya shardanta cewa wajibi ne daya daga cikin masu tsayawar ya kasance basaraken gargajiya daga garinsu Sowore da ke Karamar Hukumar Ese-Odo da ke Jihar Ondo. Mutum na biyu kuma, wajibi ne ya kasance ya mallaki gida a Abuja.
Kotun ta kara da cewa cewa wajibi ne mutanen da za su tsaya wa Sowore su samu tantancewar lauyan masu gabatar da kara, Akinlolu Kehinde, (SAN).
- Matar aure ta yi yinƙurin yi wa mijinta yankan rago a Kastina
- Manyan abubuwa 5 kan sabon tsarin NYSC
- An kama dan sanda kan yi wa ’yar shekara 13 fyade
Wajibi ne kuma wanda ake zargin, wato Sowore, ya mika takardar fasfon tafiye-tafiyensa ga kotun, kafin a yi komai.
Lauyan wanda ake zargi, R. O. Adakole, ya bukaci kotun ta bayar da izinin sakin Sowore domin ya karbo fasfo dinsa daga Ofishin Jakadancin Amurka da ke Legas.
A karshen zaman, alkalin ya dage sauraron batun zuwa ranar 6 ga watan Yuli, domin sauraron rokon lauyan Sowore.
a ranar 16 ga Yuni, kotun ta bayar da umarnin tsare Omoyele Sowore, a gidan gyaran hali na Kuje, bayan Mai Shari’a Mohammed Umar ya soke belin da ya ba shi a watan Disamba da ya gabata.