Kotu ta soke nasarar Gwamna Abdullahi Sule na Nasarawa

Bayanai sun ce biyu daga cikin alkalan uku ne suka soke nasarar Gwamna Abdullahi.

Kotu ta soke nasarar Gwamna Abdullahi Sule na Nasarawa

Gwamna A.A Sule

Kotun Sauraron Kararrakin Zabe a birnin Lafia ta soke nasarar Gwamna Abdullahi Sule na Jihar Nasarawa.

Kotun wadda alkalai uku karkashin jagorancin Mai Shari’a Ezekiel Ajayi suka yanke hukunci, ta umarci Hukumar Zabe ta Kasa INEC da ta janye shaidar lashe zabe da ta bai wa Gwamnan.

Bayanai sun ce biyu daga cikin alkalan uku ne suka soke nasarar Gwamna Abdullahi.

Wakilinmu ya ruwaito cewa, kotun ta kuma ayyana dan takarar jam’iyyar PDP, David Ombugadu a matsayin wanda ya yi nasara a zaben.

Ana iya tuna cewa, a sakamakon da INEC, ta ce Gwamna Sule na jam’iyyar APC ya samu kuri’u 347,209 yayin da abokin takararsa, Mista  Ombugadu ya samu kuri’u 283,016.

Baffa Bichi da Barau Jibrin sun gana a Abuja

MC Tagwaye ya fice daga APC zuwa SDP

Wata mata ta faɗa ruwa ta mutu a Legas

Direba ya murƙushe yarinya ta mutu a artabu da jami’an tsaro a Edo