Kotu ta tsare matashin da ya kashe kanwarsa da matar babansa

Wata kotun majisater da ke Kano ta gurfanar da matashin da ake zargi da kisan matar babansa da kanwarsa a unguwar Rijiyar Zaki.

Kotu ta tsare matashin da ya kashe kanwarsa da matar babansa

Wata kotun majisater da ke Kano ta gurfanar da matashin da ake zargi da kisan matar babansa da kanwarsa a unguwar Rijiyar Zaki.

Kotun karkashin jagorancin Mai Shari’a Talatu Makama, na tuhumar matashin ne da laifin kisan kai, wanda ya saba wa sashi na 221 na kundin Penal Code.

Lauya mai kara Barista Gazali Maigari Bichi ya roki kotun ta karanto wa wanda ake tuhuma laifukansa, inda kotun ta umarci jami’inta Ibrahim Koya ya karanto masa.

Bayan karanto masa ne kuma ya amsa laifinsa, kotun ta kuma aike da shi da gidan kaso, ta kuma dage shari’ar zuwa ranar 2-3-2023.

An kama mutum uku da ƙwato wayoyin lantarki na sata 

Zan ci gaba da bada kuɗin hadaya kyauta — Gwamna Zulum 

Obasanjo na yunƙurin ɓata min suna don ɗan takararsa — Atiku

Sojoji sun kama masu garkuwa da mutane a Yobe