Kotu ta yi fatali da karar Binani kan nasarar Fintiri a Adamawa

Kotun ta ce mai kara ta gaza gabatar da hujjojin da za su gamsar da kotun

Kotu ta yi fatali da karar Binani kan nasarar Fintiri a Adamawa

Binani da Fintiri

Kotun sauraron kararrakin zaben Gwamnan Jihar Adamawa da ke zamanta a Yola, ta yi fatali da karar da ‘yar takarar APC a zaben Gwamnan da ya gabata, Sanata Aishatu Dahiru Binani ta shigar tana kalubalantar nasarar Gwamna Ahmed Umaru Fintiri.

Binani dai ta shigar da karar ce tana so kotu ta soke nasarar da Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta ce Fintiri na jam’iyyar PDP ya samu a zaben watan Maris din da ya gabata.

Sai dai da take yanke hukunci ranar Asabar, Mai Shari’a Theodora Uloho, ta ce masu karar sun gaza  gabatar da kwararan hujjojin da za su tabbatar da da’awarsu cewa an saba wa Kundin Dokar Zabe ta Kasa ta 2022 a yayin zaben.

Fintiri dai ya lashe zaben ne da kuri’u 430,861, inda ya doke Binani mai kuri’a 398,788.

Idan za a iya tunawa, sai da aka je zagaye na biyu kafin a bayyana wanda ya lashe shi, saboda INEC ta ayyana na farko a matsayin wanda bai kammala ba.

An buƙaci mazauna Benuwe su yi ƙaura saboda fargabar ambaliyar ruwa

Abubuwan da ya kamata ku sani game da Zaɓen Edo

Ban zama Shugaban Kasa don na tara kuɗi ba — Tinubu

Babu buƙatar mu riƙa tsayar da motoci muna duba takardu — ’Yan sanda