kungiyar Tambarin Arewa ta samar da asusun tallafa wa yara

Wata kungiya  mai suna Tambarin Arewa ta ’yan Arewa da ke  zaune a Legas ta samar da asusu na musamman domin tallafa wa yaran  da ke  zaune  a cikin jihar  ta Legas, saboda ganin yadda  wasu iyaye ba su da karfi agaza wa ’ya’yansu domin samun ilmi nagartacce.kungiyar  ta ce  sau  tari  akan  samu  yara  […]

kungiyar Tambarin Arewa ta samar da asusun tallafa wa yara
kungiyar Tambarin Arewa ta samar da asusun tallafa wa yara

Wata kungiya  mai suna Tambarin Arewa ta ’yan Arewa da ke  zaune a Legas ta samar da asusu na musamman domin tallafa wa yaran  da ke  zaune  a cikin jihar  ta Legas, saboda ganin yadda  wasu iyaye ba su da karfi agaza wa ’ya’yansu domin samun ilmi nagartacce.
kungiyar  ta ce  sau  tari  akan  samu  yara  hazikai,  amma  rashin  wanda  zai  tallafa   musu   su yi  karatu,  sai  ka ga  sun fada  wata  rayuwar  da  ba ta  dace  ba,  don  haka  daga  yanzu  duk  wani  yaro haziki  da  ta  samu  labarinsa  kuma  ba ya  da  wanda  zai  agaza  masa,  za ta  dauki  nauyinsa.
Sakataren kungiyar  Barista  Isah Buhari  ya ce ta  haka  ne  za su   ba da gudunmowarsu  ga  matasa,  kuma  haka  zai  iya  kauda  su  daga  gararamba, musamman  ganin  yadda  rayuwa  take  a birnin Ikko, wadda ta sha  bamban  da  ta Arewa. ya ce muddin  ana ci gaba  da  nuna  halin ko-oho  ga harkar  ilimi,  to  ba  shakka  al’umma  ba za ta ci  gaba  ba.
Dangane da inda kungiyar  za ta  rika  samun kudin  da  za ta  yi wannan taimako,  sai ya ce  daga  harajin  da  za su  rika yi wa  su  kansu ’ya’yanta  da kuma  neman  tallafi  daga kamfanoni  masu  zaman kansu  sai kuma  bude  wajen ajiya,  wanda  za su  rika  amfana  da shi  a  bisa  tsarin  ajiya,  kwatankwacin  na  banki.
Shi ma shugaban kungiyar, Alhaji Mustafa Ibrahim  ya ce baya ga  taimaka wa  yara, kungiyar  za ta  agaza wa  masu  sana’ar  hannu, kuma  za ta  rika  wayar  musu da  kai  a kan  batun  wuraren  da  gwamnatin  jihar ta  hana  a yi  kasuwanci, lamarin da jahiltarsa ke sa su shiga  tsaka-mai-wuya  a  hannun jami’an tsaro.
Daga  karshe  kungiyar  ta ja  kunnen ’yan Arewan su kasance masu  bin doka  da oda,  wanda ta  haka ne  zamansu zai ci  gaba,  ya  yi tasiri.