Kwamishina ya yi murabus saboda takarar shugabancin APC a Kano
Doguwa ya miƙa takardar murabus ɗinsa tun a ranar Litinin, 2 ga Maris, 2026.
Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf
Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da murabus ɗin Kwamishinan Albarkatun Ruwa, Umar Haruna Doguwa, yayin da ake hasashen zai tsaya takarar shugabancin jam’iyyar APC a jihar.
Mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Talata.
- HOTUNA: Mabiya Shi’a a Najeriya na zanga-zangar goyon bayan Iran
- Tinubu ya naɗa Taiwo Oyedele Ministan Kuɗi
Sanarwar ta ce Doguwa ya miƙa takardar murabus ɗinsa tun a ranar Litinin, 2 ga Maris, 2026.
Gwamna Yusuf ya yaba masa bisa jajircewa da hidimata wa al’ummar Kano, yana mai jinjina da irin rawar da ya taka a Ma’aikatar Ilimi kafin daga bisani a mayar da shi Albarkatun Ruwa, inda aka samu ci gaba wajen gyaran rumbunan ruwa da faɗaɗa samar da ruwan sha a sassan jihar.
Sai dai majiyoyi sun ce murabus ɗin na da alaƙa da shirin Doguwa na tsayawa takarar shugabancin APC a Kano gabanin babban taron jam’iyyar da za a yi a Dandalin Wasanni na Kofar Mata.
Jam’iyyar ta ce ta kafa kwamitoci uku domin tabbatar da sahihanci da zaman lafiya a taron, tana mai jaddada ƙudirin ta na ƙarfafa dimokuraɗiyya a cikin gida da haɗin kai a jihar.