Kwankwaso ya gana da Tinubu a Fadar Shugaban Kasa

Kwankwaso ne abokin hamayya na farko da ya gana da Tinubu a Fadar Shugaban Kasa.

Kwankwaso ya gana da Tinubu a Fadar Shugaban Kasa

Rabiu Musa Kwankwaso

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya gana da tsohon Gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso a Fadar Gwamnatin Najeriya da ke Abuja.

Kwankwaso shi ne abokin hamayya na farko da Shugaba Bola Tinubu ya karbi bakuncinsa bayan sun yi adawa da juna a Zaben Shugaban Kasa wanda aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabrairun 2023.

Kazalika, Kwankwaso da Shugaba Tinubu sun yi makamanciyar wannan ganawa a birnin Paris na Faransa kwanaki kadan gabanin rantsar da Shugaban Kasar a ranar 29 ga watan Mayun da ya gabata.

Ana iya tuna cewa Kwankwaso ne ya zo ma hudu a Babban Zaben inda ya yi takara a jam’iyyar NNPP mai alamar kayan marmari.

Afirka ta Kudu ta yi martani kan korar jakadanta daga Amurka

Trump ya dakatar da kafar watsa labarai ta VOA

Mahaifiyar Sarkin Gwoza ta rasu

Yadda za a girka ‘Kamoniya’