Lai Mohammed na neman a dakatar da sabunta rijistar mambobin APC a Kwara

Ministan Watsa Labarai da Al’adu, Lai Mohammed, ya yi kira da a soke rijistar ’ya’yan jam’iyyar APC da ake gudanarwa a halin yanzu a Jihar Kwara.

Lai Mohammed na neman a dakatar da sabunta rijistar mambobin APC a Kwara

Ministan Yada Labarai da Raa Al’adu, Lai Mohammed

Ministan Watsa Labarai da Al’adu, Lai Mohammed, ya yi kira da a soke rijistar ’ya’yan jam’iyyar APC da ake gudanarwa a halin yanzu a Jihar Kwara.

Ya bayyana hakan ne a wata ganawa da ’yan jarida ranar litinin a mahaifarsa dake Oro, inda ya yi zargin cewa jami’an da aka tura don yin rijistar jam’iyyar a jihar sun karya ka’idojin da uwar jam’iyar ta kasa ta shimfida.

Ministan ya kuma ce kwamatin ya karya sharudan da aka gindaya na rarraba kayan gudanar da aikin rijistar ’ya’yan jam’iyyar a fadin jihar.

“Ka’idojin yin rijistar da uwar jam’iyyar ta shimfida a bayyane suke, kuma an haramta ba mutanen da basu da alaka da aikin kayan yin rijistar jam’iyyar su rarraba ko rike wasu muhimman takardu da foma-fomai da katinan jam’iyyar ga mutanen da ba su da ce a basu ba”

“Kayan aikin yin rijistar da suka hada da foma-fomai da kundin rijistar da katin shaidar zama dan jam’iyya wanda take jami’in yin rijistar a hukumance ne kadai ke da alhakin daukar bayanan mutum da rarraba katin kamar yadda aka tsara a hukumance,” In ji shi

Ministan ya bukaci a soke baki dayan rijistar a fadin Jihar ta Kwara har sai an tabbatar da yin rijistar kamar yadda jam’iyyar ta tsara kuma yadda kowa zai gamsu da tsarinta.