Likitoci sun janye zanga-zangar da suka shirya

Likitoci Masu Neman Kwarewa sun janye zanga-zanar gama-garin da ta shirya farawa a fadin Najeriya a yau Laraba.

Likitoci sun janye zanga-zangar da suka shirya

Kungiyar Likitoci Masu Neman Kwarewa (NARD) ta janye zanga-zanar gama-garin da ta shirya shiga a fadin Najeriya a yau Laraba.

Shugaban kungiyar, Dokta Orji Emeka Innocent, ya ce majalisar kolin kungiyar ta yanke shawarar ne bayan taron da ta yi ranar Laraba da dare.

Sai dai ya ce cikin sa’o’i 72 masu zuwa kungiyar za ta sake zama ta kara nazari kan matakin janye zanga-zanar.

Da farko NARD ta shirya gudanar da zanga-zanga a kullum ta hanyar rufe cibiyoyin lafiya mallakin gwamantin tarayya daga karfe 10 na ranar Laraba 9 ga watan Agustan nan da muke ciki.

Babu buƙatar mu riƙa tsayar da motoci muna duba takardu — ’Yan sanda

‘Yan bindiga sun ƙone gidan mai da motoci 4 a Enugu

Kwalara ta kashe fiye da mutum 300 a Sudan

A tabbatar an mutunta tsarin dimokuraɗiyya a Zaɓen Edo — Tinubu