Mace Manjo-Janar ta farko a Najeriya ta rasu
Macen da ta fara kaiwa matsayin Manjo-Janar a rundunar sojin Najeriya, da ma yankin Afirka ta Yamma, Aderonke Kale ta rasu tana da shekaru 84
Aderonke Kale ta rasu tana da shekaru 84
Macen da ta fara kaiwa matsayin Manjo-Janar a rundunar sojin Najeriya, da ma yankin Afirka ta Yamma, ta kwanta dama.
Manjo-Janar Aderonke Kale (murabus), wacce ita ce mace ta farko da ta zama kwamandar asibitin soji a Najeriya ta rasu ne a ranar Laraba tana da shekaru 84.
- EFCC ta cafke garin kudi na N11m a hannun masu sayen kuri’u
- Duk wadanda muke bi bashi sai sun biya — MTN
Kakakin rundunar, Onyema Nwachukwu ya ruwaito babban hafsan rundunar, Laftanar Janar Taoreed Lagbaja na bayyana kaduwa da rasuwar Manjo-Janar Aderonke.
Laftanar-Janar Lagbaja ya bayyana rasuwar Manjo-Janar Aderonke Kale a matsayin babban rashi ga Najeriya da ma duniyar aikin soji, inda ya bayyana yadda ta sadaukar da kanta wajen hidimta wa bil Adama, wanda ba za a taba mantawa ba.