Mace ta maka Nuhu Ribadu da kasa a zaben fidda gwanin APC a Adamawa

Sanata Binani ta maka Nuhu Ribadu da kasa da tsohon Gwamnan Jihar da kasa

Mace ta maka Nuhu Ribadu da kasa a zaben fidda gwanin APC a Adamawa

Sanata Aishatu Binani

Sanata mai wakiltar Adamawa ta Tsakiya, Aishatu Dahiru Ahmed Binani, ta maka tsohon Shugaban EFCC, Nuhu Ribadu, da kasa a zaben fidda gwani na Gwamna a jam’iyar APC a Jihar Adamawa.

Binani ta samu kuri’a 430, yayin da Nuhu Ribadu ya samu kuri’a 288.

Hakan dai na nufin Binanin ce za ta yi wa jam’iyyar ta APC takarar Gwamna a Jihar a zaben shekarar 2023 mai zuwa.

Muhammad Jibirilla Bindow, tsohon Gwamnan Jihar ya zo na uku da kuri’a 103 yayin da Abdulrazak Namdas ya zo a matsayi na hudu da kuri’a 94.

Kazalika Umar Mustapha Madawaki da Wafarniyi Theman sun zo a matsayi na biyar da na shida a zaben fidda gwanin da aka gudanar a ranar Alhamis a Jihar.