Maciji ya kashe kwamandan ’yan ta’adda a Borno

Akwai rashin kula tun bayan saran da maciji ya yi wa kwamandan.

Maciji ya kashe kwamandan ’yan ta’adda a Borno

Maciji

Daya daga cikin kwamandojin kungiyar ISWAP ya mutu a Jihar Borno, sanadiyar sarar da maciji ya yi masa.

Kwararren mai masani kan yaki da tayar da kayar baya a gabar Tafkin Chadi, Zagazola Makama ne ya tabbatar da hakan.

Makama ya ce kwamandan na ISWAP da ake kira da Kiriku, ya mutu ne a ranar Juma’a kwanaki uku bayan sarar macijin a maboyarsu da ke yankin Karamar Hukumar Damboa.

Ya ce mutuwar ta Kiriku na da nasaba da rashin kulawa tun bayan sarar da maciji ya yi masa.

Kafin mutuwarsa, Kiriku ya jagoranci kai hare-hare a yankin Jiddari da ke Chiralia, yankin da ke zaman matattarar Boko Haram da kuma ISWAP.

Haka nan ya jagoranci kai harin kwanton bauna kan jami’an sojojin da ke aiki a karkashin rundunar Operation Hadin Kai a jahar Borno.

Ban zama Shugaban Kasa don na tara kuɗi ba — Tinubu

Babu buƙatar mu riƙa tsayar da motoci muna duba takardu — ’Yan sanda

‘Yan bindiga sun ƙone gidan mai da motoci 4 a Enugu

Kwalara ta kashe fiye da mutum 300 a Sudan