Magidanci ya kashe kansa ya bar matarsa da tsohon ciki

Matsafa sun yanki gawar mutum da aka tsince ta tana lilo a jikin bishiya.

Magidanci ya kashe kansa ya bar matarsa da tsohon ciki

Wani magidanci mai shekara 45 ya rataye kansa ya bar matarsa da tsohon ciki.

Kakakin ’yan sandan Jihar Osun, Yemisi Opalola, ya tabbatar da aukuwar lamarin a ranar Talata a unguwar Oke-Opo da ke Ilesa a Jihar.

Mamacin wanda tela ne ya bar gida tun ranar Litinin ba tare da ya sanar da matarsa mai tsohon ciki ko wani inda za shi ba.

Mutanen yankin sun tsinci gawar Olatunji tana lilo ne a jikin wata bishiya.

Ana zargin matsafa sun yanki wani bangare na jikin mamacin kafin su sauke gawar daga kan bishiyar.

Wani matsafi a yankin da ya nemi Aminiya ta sakaya sunansa ya ce dole ne a yanki wani bangare na jikin gawar don guje wa faruwar wani bala’i da ka iya tasowa a gaba.

Okpebholo ya lashe zaɓen Gwamnan Edo

HOTUNA: Yadda bikin Takutaha ya gudana a Kano

Zaɓen Gwamna: APC ta kama hanyar lashe zaɓen Edo

Zaɓen Edo: INEC ta dakatar da tattara sakamako