Magidanci ya kashe mahaifiyarsa a Neja

Mahaifiyar ta gamu da ajalinta yayin da ta rabun fada tsakanin danta da mai dakinsa.

Magidanci ya kashe mahaifiyarsa a Neja

Wuka

Wani magidanci ya caka wa mahaifiyarsa wuka ya aika ta lahira sannan ya yi wa matarsa rauni da wukar.

Matashin, mai shekara 27, ya aikata danyen aikin ne bayan wani sabani da suka samu da matar tasa a garin Kontagora na Jihar Neja.

Shaidu sun ce ya luma wa mahaifiyar tasa wuka ne bisa kuskure a lokacin da dattijuwar take kokarin raba fada tsakaninsa da matarsa a yayin da ma’auratan suke ba wa hamata iska.

Matar tasa da ya yi wa raunuka da wukar kuma an kai ta Babban Asibitin Kontagora domin jinyar ta.

Wata majiya da wakilinmu ya zanta da ita, ta bayyana a sirrance cewa matashin da ya yi aika-aikan yana fama da tabin hankali.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Neja, Bala Kuryas ya tabbatar da faruwar lamarin, ya kuma ce ana gudanar da bincike a kai.

Zaɓen Edo: Yadda aka kama masu sayen ƙuri’a da ’yan daba

Sarakunan Nijar sun kai wa Gwamnatin Yobe ziyarar jaje

Ɗan majalisa ya yi jinjina kan naɗa Danyaya Sarkin Ningi

’Yan Sanda sun kama gungun ’yan fashi 7 a Katsina