Magidancin da ya kashe Jariri ya shiga hannu a Adamawa

Mahaifiyar jaririn ta samu munanan raunuka.

Magidancin da ya kashe Jariri ya shiga hannu a Adamawa

‘Yan sanda

Rundunar ‘yan sandan Jihar Adamawa ta samu nasarar damke wani magidanci da ake zargi da kashe wani jariri.

Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, SP Suleiman Yahaya Nguroje ne ya tabbatar da kama mutumin a cikin wata sanarwa da ya fitar.

Wanda ake zargi ya kashe jaririn ne a yayin da aka kai wa mahaifiyar jaririn hari a ranar 29 ga watan Satumbar 2022.

“Wanda ake zargi da kisan Barnabas Abduneza mai shekara 40, mazaunin kauyen Kpasham da ke Karamar Hukumar Demsa, ya shiga hannu ne a sakamakon samun kwakkwaran bayanai,” a cewar kakakin.

Sanarwar ta kuma ce, mahaifiyar jaririn ta samu munanan raunuka, yayin da jaririn da ta ke dauke da shi ya mutu.

Rundunar ta kuma samu wanda ake zargi dauke da miyagun makamai ciki har da wuka, da kwari da baka a lokacin da kama shi.

Sojoji sun kama masu ƙera makamai a Kebbi

Bam ya kashe aƙalla mutum shidda a Siriya

’Yan bindiga sun kashe Limami da wasu a Sakkwato

Gwamnati za ta mayar da yara 5,000 makaranta a Jigawa