Mahaifin ma’aikacin Aminiya ya rasu

Shi ne mutum na farko ɗan asalin Jihar Katsina da ya samu muƙamin Farfesa a fannin harshen Larabci.

Mahaifin ma’aikacin Aminiya ya rasu

Allah Ya yi wa mahaifin ma’aikacin Aminiya, Abubakar Abdurrahman Adoro, rasuwa.

Mahaifin nasa, Farfesa Abdurrahman Lawal Adoro, ya rasu ne a gidansa da ke garin Batagarawa a Jihar Katsina, ranar Litinin 27 ga watan Janairu, 2025, a Asibitin Koyarwa na Tarayya da ke Katsina, ya yi fama da jinya na wani lokaci.

Marigayi Shehin Malami a Sashen Harshen Larabci na Jami’ar Umaru Musa Yar’adua da ke Jihar Katsina, inda a nan ya samu matsayin Farfesa.

Ya kasance Shugaban Sashen Larabci (HOD) na Jami’ar na farko tun da aka kirkiro ta a shekarar 2006, inda ya yi wa’adi biyu na tsawon shekara goma zuwa 2016.

Shi ne mutum na farko ɗan asalin Jihar Katsina da ya samu muƙamin Farfesa a fannin harshen Larabci.

Haka kuma yana daga cikin malaman da suka ƙaddamar da Kungiyar Jama’atu Izalatul Bid’a Ka Ikamatis Sunnah (JIBWIS) a Jihar Katsina.

An haife shi a ranar 15 ga Fabrairu, 1953 unguwar Adoro da ke garin Katsina, kuma ya rasu yana da shekara 72, ya bar ’ya’ya 10 da jikoki 32.

 

MC Tagwaye ya fice daga APC zuwa SDP

Wata mata ta faɗa ruwa ta mutu a Legas

Direba ya murƙushe yarinya ta mutu a artabu da jami’an tsaro a Edo

Lakurawa: Gwamnan Kebbi ya nemi a kafa sansanin soji a jihar