Mahara sun kashe mata da kananan yara a kauyen Filato

Gwamna Lalong ya ce maharan sun kai harin ne kafin wayewar garin Talata a yayin da mutanen kauyen ke tsaka da barci.

Mahara sun kashe mata da kananan yara a kauyen Filato

Simon Lalong, Gwamnan Jihar Filato.

Ana fargabar an kashe kananan yara da mata da yawa a wani hari da aka kai a kauyen Kubat na Karamar Hukumar Mangu ta Jihar Filato.

Gwamnan jihar, Simon Bako Lalong, ya tabbatar cewa maharan sun kai harin ne kafin wayewar garin Talata a yayin da mutanen kauyen ke tsaka da barci.

Lalong ya yi Allah-wadai da harin, sannan ya umarci jami’an tsaro da su farauto mahran domin su fuskanci hukunci.

Sanarwar da daraktan yada labaran gwamnan, Makut Simon, ya fitar ta ce Lalong ya umarci hukumomin agaci da na zaman lafiya na jihar su ziyarci kuayen domin gano tantance girmar barnar  da aka yi domin samar da tallafi ga wadanda abin ya shafa.

MC Tagwaye ya fice daga APC zuwa SDP

Wata mata ta faɗa ruwa ta mutu a Legas

Direba ya murƙushe yarinya ta mutu a artabu da jami’an tsaro a Edo

Lakurawa: Gwamnan Kebbi ya nemi a kafa sansanin soji a jihar