Mahara sun kashe ’yan sanda 4 a Katsina

Maharan sun hallaka ’yan sanda huɗu tare da raunta wasu.

Mahara sun kashe ’yan sanda 4 a Katsina

‘Yan bindiga

’Yan bindiga sun kai hari wani sansanin ’yan sanda a Jihar Katsina, inda suka kashe jami’ai huɗu da wasu mutum biyu.

Sun kai harin ne sanssnin ’yan sandan kwantar da tarzoma da ke Garagi, a Karamar Hukumar Kankara.

Mazauna garin sun ce maharan sun kashe jami’an tsaro huɗu tare da raunta mutum ɗaya.

Har wa yau, maharan sun yi awon gaba da bindigogin ’yan sanda.

Kazalika, sun kashe wasu mazauna garin guda biyu.

Wani mazaunin yankin da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce maharan sun ƙone azuzuwan makarantar firamaren Tsamiyar Jino, inda jami’an tsaron suka kafa sansaninsu.

Ƙoƙarin jin ta bakin kakakin rundunar ’yan sandan jihar, ASP Abubakar Sadiq Aliyu, ya ci tura zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.

Sojoji sun kashe kwamandan ’yan bindiga da tarwatsa 300

Zaɓen 2027: Tinubu ya sake tsayar da Shettima mataimakinsa

Tinubu ya gaji yana buƙatar ya huta — Peter Obi

Ɗalibai da malamai da aka sace a Oyo sun kuɓuta