Mai kwacen waya da mota ta buge a Kano ya mutu

A safiyar nan ta Talata ce mai kwacen wayan ya ce ga garinku nan

Mai kwacen waya da mota ta buge a Kano ya mutu

Mai kwacen wayan nan da mota ta buge shi a Kano ya mutu, a cewar rundunar ’yan sandan jihar.

A safiyar nan ta Talata ce mai kwacen wayan ya ce ga garinku nan a inda aka kwantar da shi, “a Asibitin Murtala,” inji kakakin rundunar, Abdullahi Harun Kiyawa, ya sanar.

Aminiya ta ruwaito ranar Lahadi cewa mota ta mai kwacen wayan ne a lokacin yake kokarin tserewa bayan ya yi wa wata mata fashin wayarta.

Kakakin ’yan sandan jihar Kano, Haruna Abdullahi Kiyawa, ya ce mota ta kade shi ne a yayin da yake kokarin tsallaka titi bayan ya yi fashin.

A jiya, Kiyawa ya sanar cewa, “Bayan mun kai shi asibiti yana dan motsi, kashin bayansa ya karye (Spinal Code) kuma kansa ya fashe. Suna shawara su sa shi a “ICU”.”

Kwacen waya na daga cikin matsalolin tsaro da suka addabi jihar Kano, inda a wasu lokuta masu kwacen ka hallaka jama’a.

A sanadiyyar wannan matsala, gomman mutane a jihar sun rasa rayuwarsu a hannun masu kwace waya, wasa da dama kuma suka tsallake rijiya da baya da rauni ko asarar dukiya.

Lamarin ya dan yi sauki baya-bayan nan a sakamakon matakan da ’yan sanda da gwamnatin jihar suka dauka.
A wata hira a aka yi da gwamnan jihar, Abba Kabir yusuf ya sanar da afuwa da kuma shirin tallafin sana’a ga ’yan daba, wadanda da akasarinsu ke harkar kwacen waya.

Amurka ta dakatar da bai wa Afirka ta Kudu tallafi

Yadda rikicin shugabanci ya janyo rufe babban masallacin gari

Yadda Kano ke samar da madarar Naira biliyan 2.2

An dakatar da dagaci kan zargin saran maraya da adda