Majalisa ta amince da nadin sabbin Jakadun da Tinubu ya gabatar

Sabbin jakadun su ne Aminu Muhammad Dalhatu daga Jihar Jigawa da Lateef Kayode Kolawole Are daga Jihar Ogun, da kuma Emmanuel Ayodele Oke daga Jihar Oyo.

Majalisa ta amince da nadin sabbin Jakadun da Tinubu ya gabatar

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio

Majalisar Dattawa ta amince na nadin mutum uku na farko da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya gabatar mata domin tantancewa a matsayin jakadun Najeriya a kasashen waje.

Sabbin jakadun da majalisar ta amince da nadin nasu su ne Aminu Muhammad Dalhatu daga Jihar Jigawa da Lateef Kayode Kolawole Are daga Jihar Ogun, da kuma Emmanuel Ayodele Oke daga Jihar Oyo.