Majalisa ta amince Tinubu ya nada hadimai 20

Sai dai Tinubu bai bayyana sunayen wadanda zai bai wa mukaman ba.

Majalisa ta amince Tinubu ya nada hadimai 20

Majalisar Dattawa

Majalisar Dattawa ta amince da bukatar Shugaban Kasa Bola Tinubu ta nada masu ba shi shawara na musamman guda 20.

Shugaban Majalisar Dattawa, Ahmad Lawan ne ya karanta wasikar Tinubu a zauren majalisar a ranar Talata.

Sai dai a cikin wasikar da aka aike wa Majalisar Dattawan, shugaban kasar bai bayyana sunayen masu ba da shawara na musamman guda 20 ba da zai nada ba.

Amma bayan karanta wasikar, babban zauren majalisar ya amince da bukatar cikin gaggawa.

An buƙaci mazauna Benuwe su yi ƙaura saboda fargabar ambaliyar ruwa

Abubuwan da ya kamata ku sani game da Zaɓen Edo

Ban zama Shugaban Kasa don na tara kuɗi ba — Tinubu

Babu buƙatar mu riƙa tsayar da motoci muna duba takardu — ’Yan sanda