Rashin tsaro: Majalisa ta bukaci a dage kidayar 2021

Majalisar Wakilai ta bukaci Gwamnati ta dakatar da kidayar da aka shirya gudanarwa a bana.

Rashin tsaro: Majalisa ta bukaci a dage kidayar 2021

Femi Gbajabiamila, Shugaban Majalisar Wakilai.

Majalisar Wakilai ta bukaci Gwamnatin Tarayya ta dakatar da kidayar jama’a da gidaje da aka shirya gudanarwa a bana.

Majalisar ta yi kiran ne bayan dan majalisa mai wakiltar Bosso/Paikoro dag Jihar Neja, Shehu Beji ya bayyana cewa matsalolin tsaro da sauransu za su shafi sahihancin alkaluman kidayar.

Ya ce matsalar rashin tsaro da ke barazana ga ka ’yan Najeriya ya sa yawancinsu kaura daga yankunansu, wanda zai yi illa ga nasarar da ake burin cimma da aikin.

A cewarsa, baya ga haka, su kansu jami’an kidayar babu tabbacin tsaron lafiyarsu a wuraren da za su gudanar da aikin a sassan kasar inda a wasu wuraren ake fama da rikice-rikice.

Ma’aikatan Abuja ba sa sona — Wike

Boko Haram sun kai hari sansanin sojoji da ofishin ’yan sanda

Mutane Biyu Sun Mutu, Da Dama Sun Jikkata Sakamakon Ruwan Sama A Gashuwa

Gwamnati ta ƙara albashin sojoji — Ministan Tsaro