Majalisa ta kammala karatu na biyu a kan kasafin 2021
Majalisar ta gama karatu na biyu a kan kasafin mako guda bayan Buhari ya mika mata
Shugaba Buhari a lokacin da yake ajiye kudnin kasafin 2021 a zauren Majalisar Tarayya
Majalisar Dattawa ta kammala karatu na biyu a kan daftarin kasafin 2021.
Kamalla karatu na biyun na zuwa ne mako guda bayan Shuaba Buhari ya gabatar wa Majalisar Tarayya kasafin na Naira tiriliyan 13.08.
- Kasafin 2021: Noma da Arewa maso Gabas na bukatar kudade —Monguno
- Kasafin 2021: Majalisa ta bukaci a kara wa bangaren tsaro kudi
Majalisar Dattawa ta yi kwana uku tana muhawara a kan daftarin kafin ta kammala karatu na biyu a kansa.
Daga nan Shugabanta, Sanata Ahmad Lawan ya tura kasafin ga Kwamitin Kasafi na Majalisar domin ci gabda da aiki.
Ahmad Lawan ya bukaci kwamitin wanda Sanata Barau Jibrin ke jagoranta da ya kawo wa rahoto cikin mako hudu.