Majalisar Dokokin Kano ta bai wa Ganduje damar karbo bashin N10bn
Za a dasa na’urori don ingata sha’anin tsaro a Jihar
Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje
Majalisar Dokokin Jihar Kano ta amince tare da bai wa Gwamnan Jihar, Abdullahi Umar Ganduje, damar ciyo bashin Naira biliyan 10 don saka kyamarorin tsaro na CCTV a Jihar.
Ana sa ran za a yi amfani da kyamarorin ne wajen inganta sha’anin tsaro a Jihar.
Amincewar ciyo bashin ta biyo bayan takardar da Gwamnan ya aike wa majalisar, wadda shugabanta, Injiniya Hamisu Ibrahim Chidari, ya karanta a zauren majalisar yayin zamanta na ranar Laraba.
Ganduje, ya ce za a sanya na’urorin ne la’akari da barazanar tsaro da Jihar ke fuskanta musamman a baya-bayan nan.
Majalisar ta amince bayan tattauna batun tare da bada shawarwari da ‘yan majalisar suka yi a yayin zaman da ta yi.
Idan ba a manta ba, a watan Mayu 2022 ne jami’an ‘yan sanda suka cafke wata mota a Jihar makare da bama-bamai da bindigu.