Majalisar jihar Katsina ta yi sabon kakaki

A yau Litinin dan majalisar dokokin jihar Katsina daga mazabar Zango, Tasi’u Musa Maigari ya zama kakakin majalisar jihar. An dai zabi Maigari ne a  matsayin kakakin majalisar dokokin jihar bayan yin murabus din tsohon kakakin majalisar Abubakar Yahaya Kusada wanda a yanzu yake neman takarar majalisar wakilan tarayya daga mazabun Ingawa da Kusada da […]

Majalisar jihar Katsina ta yi sabon kakaki

Gwamnan Katsina, Aminu Bello Masari

A yau Litinin dan majalisar dokokin jihar Katsina daga mazabar Zango, Tasi’u Musa Maigari ya zama kakakin majalisar jihar.

An dai zabi Maigari ne a  matsayin kakakin majalisar dokokin jihar bayan yin murabus din tsohon kakakin majalisar Abubakar Yahaya Kusada wanda a yanzu yake neman takarar majalisar wakilan tarayya daga mazabun Ingawa da Kusada da kuma Kankiya.

Sabon kakakin ya dage zaman majalisar zuwa ranar 14 ga Janairu 2019.