Makabartun masu hali a Afirka

Daga Abubakar AbdurRahaman Dodo a Abuja da Ibrahim Abubakar a Legas da Isa Muhammad Inuwa a Kano Majalisar birnin Bulawuyo ta bude makabartar masu kudi, a wani wuri da ake kira Athlone West, inda ake biyan a kala Dala 500, wato daidai da Naira dubu 83, sannan bayan shekara biyar za a rika biyan rabin […]

Makabartun masu hali a Afirka
Makabartun masu hali a Afirka

Daga Abubakar AbdurRahaman Dodo a Abuja da Ibrahim Abubakar a Legas da Isa Muhammad Inuwa a Kano

Majalisar birnin Bulawuyo ta bude makabartar masu kudi, a wani wuri da ake kira Athlone West, inda ake biyan a kala Dala 500, wato daidai da Naira dubu 83, sannan bayan shekara biyar za a rika biyan rabin kudin, a matsayin haya, wato kashi hamsin cikin dari (Naira dubu 41da 500).
Majalisar mulkin wannan birnin ta yi hasashen samun akalla Dala miliyan hudu da dubu 700, inda aka samu nasarar sayar da kaburbura dubu takwas da 256.
Daraktar Kula da sashen Kula d alafiya, Zanele Hwalima, ta ce, sabanin sauran birane, Bulawayo bai taba samar da wata makabarta ta kasuwanci ba, alhali ofishinta na sane da cewa, akwai mkabartar ’yan kasuwa mai zaman kanta a Harare, babban birnin Zimbabwe.
Ta ce, wannan makabarta za a samar mata duk kayan da ak bukata, wadanda suka hada da wayoyin Katanga da kofar shia da fitilu, sannan za a tabbatar da tsaro.
Wakilanmu sun bi kadin yadda ake binne mamata a wadannan makabartu. Ga yadda al’amarin ya kasance:

Akwai makabartar masu kudi a Legas
A  birrnin ikko  akwai  makabarta  mallakar  gwamnati, akwai kuma  na  masu  zaman  kansu,  wadanda  ’yan kasuwa  ko    kamfanoni  ke da  su,  kuma  kudi  masu  tarin  yawa  ne  ake  biya  kafin  a  sayar don  mallaki rami  guda  da  za ka  binne  gawa  ciki.
Akwai  wadannan makabartun  a  wuraren da suka hada da   Lekki da  Ikoyi  da  Yaba,  wadanda  duka  mallakar  wasu  mutane  ne,  kuma   sun sayi  filin  ne  daga  hannun  gwamnati,  don  haka  ba  wani   haraji  da  suke  biya,  sai  dai lokaci-lokaci  akan   bukaci  su  bayar da  gudunmuwar su,  wajen  aikin  gayya  na  unguwannin  da    makabartun  suke,  idan  bukatar  hakan  ta  taso.
Bambancin   wadannan  makabartun  da  na  gwamnati,  domin idan  ka je na    gwamnati,  musammam  a birnin  Ikko,  abu na  farko  da ke  maka  maraba  da  zuwa  shi ne  ciyawa,  wani  wurin ma ko da  kudi  aka  hada ba  za ka yarda  ka  shiga ba,  kila  wannan yasa  ake  da  mutane  a  cikin su,  koda yaushe, domin wanda  ya zo  neman  binne  gawa  ya  biya  su  kudi,  su  sare  masa   haki a  inda  aka  bashi  fili.
Shima  na  gwamnatin  ana  biya,  amma  ba  abu  ne  da  ya  taka  kara  ya  karya  ba,  sabanin  na  kudi,  wanda  yake  a  wadannan wuraren  da ke  da  wadannan makabartan  anan  cikin  birmin  Ikko,  ba  inda  yake  kasa  da Naira  miliyan   biyu, sai  dai  wajen  tas-tas  yake  kai  ka ce  ba  makabarta  ba ce,  sai  domin cewa   za ka  ga  gini  irin  na  binne  mutum,  amma  baya  ga  haka,  akwai  inda  za ka  iya  sa  tabarma  ka  kwanta  hankalin ka kwance.
Misali  makabartan  EBONY da ke  unguwar  Yaba,  a kan  titin  zuwa  jami’ar Legas,  ana  sayar  da  rami  daya  na  binne  gawa  a kan  Naira  miliyan  biyu  ne,   kuma  akwai  na  miliyan  biyar,  amma a  bisa  tsarin  yadda  ake  binne  mutane,  shi ne   kowane  rami  ana  sa  mutane uku  ne, wato  ana yi  wa  kowane  rami  matakali  ko  kuma  hawa-hawa  har  ukku, suna  kiran  sa  kabarin iyali.
Ana  iya  binne  mutum  guda,  kana  a bar  filin mutane  biyu  da  suke  daga  iyalin  guda. Sai  kuma  wani  lokaci  idan wani  ya  mutu  daga  cikin  wadannan iyalan  sai  a kara  binne  mutum  guda,  har  sai  sun kai  su  ukku;  sai  dai  idan mutum  daya  ake  so  cikin  rami  guda,  ana  iya  yin  hakan,  kuma  tunda  yake  na  sayarwa  ne,  ana  sayarwa  kowanne  irin  addini, ko  musulmai  ko kirista  koma  wadanda  ba su  da  addini.
Su kuwa  na Naira miliyan biyar,  bambancin  su  da na  miliyan biyu,  shi ne,  su  suna  cikin rumfa  ne,  ta  yadda  ruwa  ba  zai  zuba  kansu ba; kuma  ba  matacce  ba,  har  ma  mai  rai  na  iya  fake  ruwa  ko  rana  cikin  wannan rumfar. Sannan a  sauran  makabartun,  wato  na  bAULT  GARDEN  da ke  Ikoyi,  ana  samun na Naira  miliyan  daya  da  rabi.

‘Akwai bangaren kwarori daban da na sauran mutane a makabartarmu’ – Wakilin Titin Katsina
A birnin Kano da kewaye an samu makabartar da ake binne kwarori ’yan asalin kasar Lebanon a gefe daya daban, sauran mutanen gari kuma musamman Hausawan da suka rasu ake binne su a daya gefen daban. Hakan kuma ya yi kama da makabartar Kabarin Raka da ke a unguwar Gama, ta yankin karamar Hukumar Nassarawa a yankin birnin Kano da kewaye.
Dagaci ko wakilin yankin Titin Katsina a Kano, kuma wanda makabartar sansanin alhazai ke karkashin yankinsa, Alhaji Sani Sambo kaura ya tabbatar wa Amniya cewa, tabbas da akwai bangaren kwarori daban da sauran bangaren mutanen gari a wannan makabartar.
 “A sanina akalla wannan makabartar za ta kai shekara 100 da fara binne mutane a cikinta, kamar yanda na samu labarin daga mahaifina. Akwai bangare biyu, inda kwarori suke binne mutane da kuma inda sauran jama’a suke binne wa, amma kuma daga bisani kowa yana binne wa a kowane bangaren na makabartar,” inji shi.
Ya ce sai dai kwarorin sun fi binne wa a wannan bangaren da ake ganin nasu ne.
Ya musanta bayanin da wasu ke yi, cewa, ana bambanta tsakanin talakawa da masu kudi wajen binne gawa a makabartar, inda ya ce wannan maganar ba gaskiya ba ce, domin “kowa da kowa ya na binne wa da talakawa da masu kudi da malamai da kowa da kowa.”
Ya ce idan ma har da wani bambanci, bai wuce na tsakanin yanayin kaburburan kwarorin da na sauran jama’a ba.
A cewarsa: “Idan an haka kabarin ana mayar da kasar a rufe, wasu kuma suna bin gefen kabarin su gyara da sumunti ko marmara, amma su kwarorin kuwa za ka ga sun yi masa wani kyale-kyale kama da Tayil da kuma roduka na rila, su kewaye kabari.”
Ya ce akalla kwarorin sun kai shekaru 40 da fara binne mutanensu a wajen.
Ya ce gyara gefen da ake yi da marmara don kada ya baje ne, sannan kuma wadansu suna kafa alluna da rubutu game da mamaci a gefen kabarin, kamar yadda su ma kwarorin suke rubutu a jikin allon kabarin, inda ya ce makabartar tana da masu haka da masu kula da ita, kamar sauran makabartu; da masu kai ziyara, inda su ma kwarorin sukan kai ziyara, musamman a ranakun Alhamis da Juma’a.
“Ni dai a sanina ban san ana sayar da wajen ba, amma abin da na sani suna biyan mai haka, ya haka musu kabarin. Mutanenmu ma wani lokacin yakan ce a biya shi dubu biyu ko dubu daya”
Shi kuwa wani mai hakan kabari a makabartar mai suna Sharu Baita, wanda ya ce ya kai shekaru 45 yana aikin hakar kabari a makabartar, ya ce
A cewarsa: “Tarihin wannan makabarta, makabarta ce mai albarka wacce kowa yake son ya zo, kuma ana kawo manya-manyan mutanen da suka rasu a nan, kuma a kullum yini ake yi ana ziyara ta bayin Allah a nan.”
Ya ce daya bangaren na kwarori ne, kuma duk inda aka ga Tayil na kwarori ne, amma daya bangaren waje ne da ake binne manyan mutane da suka hada da Sheikh Tijjani ‘Yanmota da Sheikh Haruna Rashid Fagge da su Sheikh Manzo Arzai da Sheikh Malam Tijjani Zangon Barebari da sauran manyan malamai da Sharifai duk a nan aka binne su.
Da Aminiya ta so ta jin ko hakan ne ya sa ake ganin kamar ta manyan mutane ce, sai ya ce ko kadan ba haka ba ne. Ya kara da cewa dalilin da ya sa kwarori ke binne mutanensu a wajen shi ne, saboda su suka tambayi izini daga Marigayi Sarkin Kano Muhammadu Sunusi na I, kuma aka ba su izini su rinka binne wa a wajen.
Da Aminiya ta tambaye shi adon da ake yi wa kaburburan, sai ya ce “a’a ni iyakacina haka ne nawa, amma su suke kawo masu gininsu da komai da komai a yi musu kuma duk wanda ya ce ana sayar da wajen binne mutane a nan karya yake yi.”
Ya ce, sai dai idan ya haka kabarin akan kawo abin sadaka a ba shi, wannan shi ne kawai abin da ya sani. Ya kuma ce yana bukatar gwamnati ta taimaka musu a bisa gudummawar da suke bayarwa ta sadaukar da rayuwarsu wajen hakan kabari.