Malaman addini sun shirya wa matasa bitar zaman lafiya a Yobe

An yi kira ga matasa da su yi riko da kyawawan dabi’u daga koyarwar Annabi Muhammad SAW.

Malaman addini sun shirya wa matasa bitar zaman lafiya a Yobe

Malaman addini a Jihar Yobe tare da hadin gwiwa da ma’aikatar kula da addini ta jihar sun yi wa matasa bita kan wajabcin wanzar da zaman lafiya da sulhu da juna a tsakanin kungiyoyin Musulunci daban-daban a jihar.

Wannan taro na hadin kai a tsakanin matasa mabiya kungiyoyin addinai daban-daban an gudanar da shi ne a cibiyar addinin musulunci ta tunawa da Marayu da ke garin Nguru.

A yayin taron an yi wa matasan bita kan batutuwa da dama musamman halin kirki, hakuri, da kyawawan dabi’u wajen zama da juna musamman a tsakanin kungiyoyin musulunci daban-daban.

Shugabannin Addinin da suka jagoranci taron yi wa matasa bitar a Yobe.

An yi kira ga matasa da su yi riko da kyawawan dabi’u daga koyarwar Annabi Muhammad SAW wajen gudanar da huldar su da juna a matsayin ’yan uwan da musulunci ya hada su.

Daga cikin manyan baki da suka halarci taron akwai, Mai Martaba Sarkin Machina, Alhaji Bashir Albishir Machina, a matsayin babban bako na musamman da kuma tsohon Shugaban Jam’iyyar APC na jiha, Sani Inuwa Nguru, Shugaban Karamar Hukumar Nguru da sauransu.

KADVS ta daƙile yunƙurin sace yara da ceto wasu a Zariya

Gwamnatin Tinubu na yunƙurin hana ni yin takara — Peter Obi

An gurfanar da ƙarin mutum 17 bisa zarginsu a kisan malama

An kama matashi ɗauke da hannun mutum da bindigogi