Manchester City ta lashe Gasar Zakarun Turai karon farko a tarihi

A bana City ta yi wa duk sa’o’inta zarra a duk gasannin da ta haska.

Manchester City ta lashe Gasar Zakarun Turai karon farko a tarihi

Manchester City ta lashe Gasar Zakarun Turai karon farko a tarihi bayan shekara sama da 140 da kafuwar kungiyar.

City ta cimma wannan kadami ne bayan ta lallasa kungiyar Inter Milan da ci daya mai ban haushi a wasan karshe na babbar gasar tamaular ta Turai ajin kungiyoyi.

Dan wasan tsakiyar City na kasar Sifaniya, Rodri Hernandez ne ya jefa kwallo daya tilo a wasan wadda ta zama mafi muhimmanci a tarihin kungiyar.

Tun ba yanzu ba dai an yi hasashen cewa City ce za ta yi nasara a wasan la’akari da yadda ta yi wa sa’o’inta zarra duk gasanni da ta haska a kakar wasanni ta bana.

City ta taka rawar gani a wannan kaka wajen lashe manyan kofuna uku, da suka da Firimiyar Ingila da kofun kalubale FA sai kuma na zakarun Turai.

’Yan wasan na Pep Guardiola a yanzu sun taddo tarihin da Manchester United ta taba kafawa a shekarar 1999 na lashe dukkanin manyan kofuna 3 da suka fafata.

City ta dade tana fatan samun nasarar lashe gasar, inda a shekarar 2021 ta kai wasan karshe amma sai dai hakar ta bata cimma ruwa ba domin kashi ta sha a hannun Chelsea.

A shekarar da ta gabata ma dai, Manchester City ta yi yunkunrin kaiwa wasan karshe inda Madrid ta taka mata birki a matakin kusa da na karshe.

Trump zai tuntuɓi Putin kan yaƙin Ukraine

Madalla da hutu ga ’yan makaranta domin azumi

Tsohuwar ɗaliba ta kai ƙarar makarantar da ta kammala

Gidauniyar Dangote ta ƙaddamar da rabon abincin N16bn ga talakawan Nijeriya