Maniyyatan da za su je Hajji a jirgin farko sun yi hatsari

Motar maniyyatan ta yi hatsari ne a ranar Laraba a kan hanyarsu ta zuwa Abuja inda za su hau jirgin farko a ranar Alhamis.

Maniyyatan da za su je Hajji a jirgin farko sun yi hatsari

Maniyyatan aikin Hajjin bana daga Jihar Nasarawa da ke shirin tafiya a jirgin farko sun yi hatsari.

Rahotanni sun nuna mutum hudu sun samu rauni bayan motar maniyyatan ta yi adungure da su ne a ranar Laraba a kan hanyarsu ta zuwa Abuja inda za su hau farko a ranar Alhamis.

Hatsarin da ya ritsa da bas mai daukar mutum 18 da suke ciki ne a yankin Kara da ke Karamar Hukumar Keffi a Jihar Nasarawa.

 

Amurka za ta sayar wa Saudiyya makaman dala biliyan 1.96

Majalisar Ukraine ta amince da sabuwar gwamnati

Salihu Lukman ya fice daga Jam’iyyar ADC

Kotu ta hana FRSC tare motoci a titunan Kano