Marasa aiki sun karu a Najeriya – Rahoto

Wani sabon rahoto da Hukumar Kididdiga ta kasa wato NBS ta fitar, ya nuna cewa yawan marasa aiki ya karu a Najeriya, inda yanzu yawan marasa aikin suka kai kimanin miliyan 17 a bana, wanda hakan ya nuna cewa an samu karin kashi biyar cikin 100 na rashin aikin yi. Sannan kuma rahoton ya nuna […]

Marasa aiki sun karu a Najeriya – Rahoto

Wani sabon rahoto da Hukumar Kididdiga ta kasa wato NBS ta fitar, ya nuna cewa yawan marasa aiki ya karu a Najeriya, inda yanzu yawan marasa aikin suka kai kimanin miliyan 17 a bana, wanda hakan ya nuna cewa an samu karin kashi biyar cikin 100 na rashin aikin yi.

Sannan kuma rahoton ya nuna cewa tabarbarewar tattalin arziki da kasar ta shiga, zai iya zama babban dalilin da ya jefa kasar cikin wannan hali,  sannan kuma za a iya yin kimanin shekara daya kafin a samu sauyi daga yanayin.