Masu dauke da Coronavirus a Najeriya sun zama 214
Hukumar Yaki da Cututtuka Masu Yaduwa ta Najeriya (NCDC) ta ce an samu karin mutum biyar da aka tabbatar sun kamu da cutar Coronavirus a Najeriya, lamarin da ya sa yanzu jimillar wadanda suka kamu ya zama 214. A wani sako da ta wallafa a shafinta na Twitter, hukumar ta ce, “Zuwa karfe 10:10 na […]
Kwalba dauke da Sanfurin gwajin Coronavirus
Hukumar Yaki da Cututtuka Masu Yaduwa ta Najeriya (NCDC) ta ce an samu karin mutum biyar da aka tabbatar sun kamu da cutar Coronavirus a Najeriya, lamarin da ya sa yanzu jimillar wadanda suka kamu ya zama 214.
A wani sako da ta wallafa a shafinta na Twitter, hukumar ta ce, “Zuwa karfe 10:10 na daren 4 ga watan Afrilu, akwai mutum 214 da aka tabbatar sun kamu da COVID-19 a Najeriya”.
Mutum uku daga cikin sabbin kamuwar a jihar Bauchi suke, mutum biyu kuma a Yankin Babban Birnin Tarayya.
An dai sallami mutum 25 da suka warke yayin da hudu suka rasu sanadiyyar cutar .